
Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazak ya karbi mutane 163 wanda gamayyar jami’an tsaro suka samu nasarar kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane.
Rundunar sojan Najeriya ce ta mikawa gwamnan mutanen ranar Juma’a a birnin Ilorin. Abdulrahman ya taya shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu murnar nasarar da aka samu da kubutar da mutanen.
Gwamnan ya kuma yabawa gamayya jami’an tsaro kan haɗin kai da kuma jarumtakar da suka nuna tare da jajircewa wajen inganta tsaro da zaman lafiya a jihar.
A ranar Laraba gwamnatin jihar ta sanar da cewa jami’an tsaron sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su daga ƙauyukan Wuro da Nuku a karamar hukumar Kaiama ta jihar.

