’Yan Sanda Sun Daƙile Hare-Haren ’Yan Bindiga, Sun Ƙwato Dabbobi 452 A Sakkwato



Rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ta daƙile hare-haren ’yan bindiga tare da ƙwato dabbobi 452 da aka sace a wasu ƙauyuka na jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Ahmad Rufa’i, ya ce an ƙwato dabbobi 281 da suka haɗa da shanu 195, tumaki 84 da raƙuma biyu a Horo Birni da Marake da ke ƙaramar hukumar Shagari.

Ya ce ’yan bindigar sun shiga ƙauyukan tare da yin harbe-harbe kafin jami’an tsaro, tare da haɗin gwiwar sojoji, suka tunkare su. Bayan musayar wuta, maharan sun tsere zuwa daji, inda suka bar dabbobin da suka sato.

Rundunar ta ce mutane biyu sun samu raunuka sakamakon harbin ’yan bindiga kuma ana kula da su a asibiti.

A wani hari da aka kai ƙauyen Maikujera a ƙaramar hukumar Rabah, ’yan bindigar sun kuma sace dabbobi 171, waɗanda jami’an tsaro suka samu damar ƙwato su bayan maharan sun tsere.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Hayatu Hassan Shaffa, ya yaba wa jami’an tsaro kan ƙoƙarin da suka yi wajen daƙile hare-haren da kuma dawo da dabbobin da aka sace.

Ya kuma buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro haɗin kai domin yaƙi da ayyukan ’yan bindiga.

More from this stream

Recomended