Yan sanda sun ceto ɗaliban firamare 2 daga cikin 6 da aka sace a Nasarawa

Rundunar yan sandan jihar Nasarawa ta ce jami’anta sun samu nasarar ceto yara biyu daga cikin ɗaliban firamaren dake Alwaza a karamar hukumar Doma ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar,Ramhan Nansel shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Kafar yada labarai ta Arewa.ng ta bada rahoton yadda wasu yan bindiga suka sace ɗaliban makarantar firamaren su 6 da safiyar ranar Juma’a.

Nansel ya ce an ceto yaron nan a kauyen Sabon Kwara dake karamar hukumar Obi ta jihar inda suke samun kulawa a asibiti.

Ya kara da cewa ana cigaba da kokarin ceto sauran yaran huɗu da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...