
Rundunar ƴan sandan jihar Oyo ta ce wasu ƴan bindiga sun kai farmaki ofishin yin fasfo na hukumar shige da fice ta Najeriya dake garin Ogbomoso na jihar Oyo inda suka ɗauke bindiga da harsashi da wasu kayayyaki masu muhimmanci.
A wata sanarwa ranar Laraba, Ayanlade Olayinka mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Oyo ya ce yan bindigar sun jikkata jami’an hukumar shige da ficen su biyu dake bakin aiki a lokacin harin.
Olayinka ya ce wani babban jami’in hukumar dake lura da ofishin ne ya yi kwarmaton cewa yan bindiga sun mamaye harabar ofishin da ƙarfe 08:45 na dare
Bayan samun rahoton ne aka yi saurin tura ƙarin jami’ai zuwa wurin domin kai ɗauki tare da duba halin da ake ciki.
Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa mutane biyar daga cikin maharan ne suka haura katanga suka shiga ofishin da ya yi iyaka da wani daji nan take kuma suka farma ma’aikatan biyu dake aikin dare.
Mai magana da yawun rundunar ya ce maharan sun lakadawa jami’an duka da sanda da kuma wasu muggan makamai kafin su yi awon gaba da bindigar ofishin ƙirar G3 da harsashinta.
Olayinka ya ce maharan sun kuma kwace wayar hannu ta ɗaya daga cikin jami’an tare da ɗauke injin janareta da kuma batirin babur.
Ya kara da cewa an kai jami’an da suka jikkata a asibiti kuma suna cigaba da samun sauki.
Harin na zuwa makonni bayan da wasu yan bindiga suka sace dalibai sama 40 daga wasu makarantu dake garin na Ogbomoso.

