
Gwamnatin jihar Kogi ta ce jami’an tsaro sun ceto mutane huɗu da aka yi garkuwa da su daga wata cibiyar zana jarrabawa dake Olowa a karamar hukumar Dekina ta jihar.
Kingsley Fanwo kwamishinan yaɗa labarai na jihar a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis ya bayyana cewa an samu nasarar kuɓutar da mutanen ne bayan wani farmaki na haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnan jihar Ahmad Ododo ya umarta da a ƙaddamar jim kaɗan bayan samun rahoton faruwar lamarin.
Fanwo ya ce Ododo ya umarci Jerry Omodara mai bashi shawara akan harkar tsaro da ya hada kan jami’an soja, yan sanda, DSS da kuma yan bijilante inda suka ƙaddamar da aikin ceto mutanen.
Da maraicen ranar Talata ne yan bindiga su ka yi garkuwa da mutanen huɗu daga makarantar sakandare ta Olowa dake karamar hukumar Dekina.
Shugaban makarantar da kuma ma’aikacin wucin gadi na hukumar shirya jarabawar kammala sakandare ta NECO na daga cikin waɗanda aka yi garkuwar da su.
Fanwo ya ce an kuɓutar da dukkanin mutane huɗu kuma suna cikin koshin lafiya.

