
Gwamnatin jihar Kwara ta ce an sako mutanen da aka yi garkuwa da su daga ƙauyukan Woro da Nuku a karamar hukumar Kaiama ta jihar
Olayinka Fafoluyi mai taimakawa gwamnan jihar, Abdulrahman Abdulrazak kan kafofin yaɗa labarai shi ne ya sanar da haka a cikin wani sako da ya wallafa shafinsa na Facebook.
“Alhamdulillah godiya ga shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, jami’an tsaro da kuma duk wanda ya taka rawa wajen samun wannan babbar nasara muna godiya,” Fafoluyi ya rubuta.
A dauke mutanen ne a ranar 3 ga watan Fabrairu lokacin da wasu mahara suka kai farmaki lokaci ɗaya kan ƙauyukan Woro da Nuku da kuma geweyensu a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar.
Mutane. 75 ne suka mutu a farmakin da maharan suka kai a yayin da wasu dama suka tsere daga muhallinsu.
Duk da da cewa har kawo yanzu ba a san yawan mutanen da aka yi garkuwa da su ba amma wasu rahotanni sun bayyana cewa mutanen da aka yi garkuwa da su sun kai su 175.
A wani fefan bidiyo da aka saka a cikin watan Afrilu an nuna ɗaya daga matan da aka yi garkuwa da su tana rokon gwamnatin jihar Kwara ta taka maka ta kubutarsu.
Babu wani bayani da aka fitar kan ko an biya kuɗin fansa da kuma yadda aka yi aka sako mutanen.

