
Mutane biyu sun rasa rayukansu bayan da wani mamakon ruwan sama da ya haifar da ambaliyar ruwa a wani ɓangare na garin Damaturu babban birnin jihar Yobe.
Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Yobe ce ta tabbatar da faruwar haka a a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata.
Mutanen da suka rasu sun hada da Isa Haruna mai shekaru 38 wanda aka fi sani da Matari sai kuma Abba Kyari mai shekaru 18 wanda ya nutse a ruwa a yankin Pompomari.
A cewar hukumar an samu ambaliyar ruwa a unguwar Malari da Pompomari da kuma geweyensu biyo bayan mamakon ruwa sama da aka yi da daren ranar Litinin.
Hukumar ta ce jami’anta na aikin ceto tare da haɗin gwiwar jami’an hukumar kashe gobara ta jihar sun hanzarta isa wurin bayan da suka samu kiran kai daukin gaggawa amma sun tarar da mutanen sun mutu kafin isarsu.
Hakan ya sa jami’an su ka tafi da gawarwakin ya zuwa sashen hatsari da bada agajin gaggawa na Asibitin General Sani Abacha dake Damaturu.

