Yan bindiga sun kashe mutane 7 a cikin masallaci a Kaduna

Akalla mutane 7 aka kashe a ranar Juma’a lokacin da wasu yan bindiga suka kai hari kan wasu masallata a kauyen Saya-Saya dake karamar hukumar Ikara ta jihar Kaduna.

Mansir Hassan mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce an kai harin ne da misalin karfe 08:00 na dare lokacin da mutanen suke sallar isha’i.

Hassan ya ce yan bindigar sun harbe mutane 6 a kauyen Saya-Saya inda suka karasa kauyen Tashar Dauda suka kashe karin wani mutum guda a masallaci.

Ya ce mutane uku sun samu rauni a lokacin farmaki kuma yan bindigar sun yi awon gaba da babura huɗu.

Mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan ya ce maharan sun samu nasarar tserewa kafin jami’an tsaro su karasa wurin da lamarin ya faru.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]