Yan bindiga sun kashe mutane 7 a cikin masallaci a Kaduna

Akalla mutane 7 aka kashe a ranar Juma’a lokacin da wasu yan bindiga suka kai hari kan wasu masallata a kauyen Saya-Saya dake karamar hukumar Ikara ta jihar Kaduna.

Mansir Hassan mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce an kai harin ne da misalin karfe 08:00 na dare lokacin da mutanen suke sallar isha’i.

Hassan ya ce yan bindigar sun harbe mutane 6 a kauyen Saya-Saya inda suka karasa kauyen Tashar Dauda suka kashe karin wani mutum guda a masallaci.

Ya ce mutane uku sun samu rauni a lokacin farmaki kuma yan bindigar sun yi awon gaba da babura huɗu.

Mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan ya ce maharan sun samu nasarar tserewa kafin jami’an tsaro su karasa wurin da lamarin ya faru.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]