Sojoji Sun Kama Wanɗanda Ake Zargi Da Safarar Makamai, Kuma Sun Ƙwato Bindigogi 7 A Kaduna


Dakarun Sashe na 7 na Sojin Najeriya sun kama wasu da ake zargin masu safarar makamai tare da ƙwato bindigogi 7 ba bisa ƙa’ida ba a wani samame da suka gudanar a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce an tare motar da ake zargin tana ɗauke da makaman ne a shingen bincike na Samaru da ke Ƙaramar Hukumar Zangon Kataf, bayan jami’an tsaro sun samu sahihan bayanan sirri.

An ce ana zargin an taso da makaman ne daga Jihar Filato zuwa Jihar Neja, kuma an yi imanin za a kai su hannun ƴan bindiga.

Har yanzu hukumomin tsaro ba su bayyana sunayen mutanen da aka kama ba, yayin da bincike kan lamarin ke ci gaba.

More from this stream

Recomended