Matasa daga jihar Kogi sun bawa Tinubu miliyan 100 ya sayi fom ɗin takarar zaben 2027

Gwamnan jihar Kogi, Usman Ododoh ya jagoranci wasu matasa daga jiharsa inda su ka mikawa jam’iyar APC naira miliyan 100 kuɗin fom ɗin takarar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben 2027.

Kuɗin ana sa ran za su sayi fom ɗin takarar shugaban ƙasa da kuma biyan kuɗin na gani ina so  a lokacin zaben fidda gwani.

Da yake karbar cak din banki na kuɗin shugaban jam’iyar APC na kasa, Nentawe Yilwatda ya shawarci sauran ƙungiyoyin dama dai-daikun mutane dake da tunanin sayawa shugaban kasa Tinubu fom ɗin saka tsayawa takara da su jingine wannan batu a gefe.

Ya ce ƙungiyar daga jihar Kogi su ne na biyu da suka nuna sha’awar sayawa shugaban ƙasa fom ɗin takarar.

Amma kuma ya ce har yanzu kungiyar ta farko basu bayar da kuɗi ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]