Adeleke Ya Ce Tinubu Ya Taya Shi Murnar Nasarar Zaɓen Osun

Muhammadu SabiuHausa37 minutes ago



Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya bayyana cewa Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya kira shi domin taya shi murnar nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar.

Adeleke ya bayyana hakan ne yayin da yake gode wa Tinubu kan abin da ya ce shi ne tabbatar da gudanar da zaɓen cikin tsarin dimokuraɗiyya.

Gwamnan ya sake lashe zaɓen bayan ya doke ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, lamarin da ya ba shi damar ci gaba da jagorantar jihar Osun na wani wa’adi na shekaru huɗu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...