Mutum Biyar Sun Mutu A Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Neja



Mutum biyar sun rasa rayukansu bayan da wani kwale-kwale ya kife a Kogin Kudi da ke ƙauyen Shaba Woshi, a ƙaramar hukumar Katcha ta jihar Neja.

Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce jami’anta sun isa wurin bayan samun rahoton hatsarin.

A cewar rundunar, an gano gawarwakin dukkan mutanen biyar daga kogin tare da gudanar da jana’izarsu.

A halin yanzu, Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Minna na gudanar da bincike domin gano musabbabin hatsarin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...