Adeleke Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Osun

Muhammadu SabiuHausa58 minutes ago



Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar na 2026.

Adeleke, wanda ya tsaya takara a ƙarƙashin Jam’iyyar Accord, ya samu ƙuri’u 511,067, yayin da babban abokin hamayyarsa na Jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, ya samu ƙuri’u 444,815.

Wannan ya bai wa Adeleke tazarar ƙuri’u 66,252 a kan Oyebamiji. Dan takarar African Democratic Congress (ADC) kuma ya zo na uku da ƙuri’u 17,180.

Da yake bayyana sakamakon, babban baturen zaɓen, Shugaban Jami’ar Tarayya ta Oye-Ekiti, Farfesa Joshua Ogunwole, ya tabbatar da cewa an kammala tattara sakamakon ƙananan hukumomi 30 na jihar.

Adadin masu kaɗa ƙuri’ar da aka tantance ya kai 1,010,684 daga cikin masu rajista 2,339,544. Daga cikin ƙuri’u 1,005,800 da aka kaɗa, an tabbatar da ingancin 985,079, yayin da aka soke 20,721.

Nasarar ta bai wa Adeleke damar ci gaba da zama gwamnan Osun, yayin da magoya bayansa suka fito kan tituna domin murnar sakamakon zaɓen.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...