Yan bindiga sun bude wuta kan ayarin motocin Ademola Adeleke gwamnan Osun

Sulaiman SaadHausa31 minutes ago

An shiga tashin hankali da fargaba a garin Osogbo na jihar Osun a ranar Laraba bayan da wasu bata gari suka kai hari kan ayarin motocin gwamnan jihar, Ademola Adeleke bayan da ya kai ziyara fadar, Jimoh Oyetunji  Ataoja na Osogbo.

Adeleke ya kai ziyara fadar sarkin ne domin nuna masa  takardar shedar lashe zaɓe da hukumar INEC ta bashi biyo bayan nasarar da ya samu a zaɓen gwamna da aka gudanar na ranar Asabar 15 ga watan Agusta.

Gwamnan ya isa fadar sarkin ne da misalin karfe 03:15 na rana cikin ayarin motoci guda 20. Amma kuma sai aka ruwaito cewa wasu batagari sun buɗe wuta kan ayarin motocin abin da ya haifar da musayar wuta tsakaninsu da jami’an tsaro dake bawa gwamnan kariya.

Rahotannin sun bayyana cewa an ɗauki kusan mintuna 12 zuwa 15 ana musayar wuta jim kaɗan bayan da basaraken ya yiwa gwamnan addu’a.

A cewar jaridar the Punch, Kolapo Alimi kwamishinan yaɗa labarai ya tabbatar da faruwar lamarin amma kuma ya ce jami’an tsaron gwamnan sun dakile harin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...