Adeleke ya ziyarci  Tinubu a fadar Aso Rock

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu a ranar Alhamis ya yi wata ganawa da Ademola Adeleke gwamnan jihar Osun a fadar Aso Rock dake Abuja.

Adeleke wanda aka sake zaɓa karo na biyu a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar ya isa fadar shugaban ƙasar da misalin karfe 05:20 na yamma inda ya zarce kai tsaye ofishin shugaban ƙasar inda suka shiga ganawa.

A yayin ganawar Adeleke ya gabatarwa da shugaban ƙasar takardar shedar cin zaɓe da hukumar INEC ta bashi.

Adeleke wanda ya yi takara karkashin jam’iyar Accord  ya samu kuri’a dubu 511, 067 a yayin da babban abokin hamayyar, Bola Oyebamiji na jam’iyar APC ya samu kuri’a dubu 444,815.

Har kawo yanzu jam’iyar APC a jihar Osun ta ki amincewa da sakamakon zaɓen gwamnan ballantana ta taya Adeleke murnar nasarar da ya samu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...