Jami’an tsaro sun kuɓutar da dukkanin yara 24 da aka ɗauke daga wani gidan marayu a Lokoja

Gwamnatin jihar Kogi ta ce an kubutar da dukkanin yara 24 da aka ɗauke daga makarantar gidan marayu ta Darul-Kitab dake Lokoja.

Gwamnatin ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba ta bakin kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Kingsley Fanwo.


Fanwo ya bayyana cewa sauran daliban 9 sun samu yancin kansu ne da tsakar daren ranar Laraba biyo bayan wani farmaki da jami’an tsaro su ka kai wa masu tsare da su.

A ranr 27 ga watan Afrilu ne yan bindiga su ka farma gidan marayun inda su ka sace yara 24 tare da matar mamallakin gidan marayun.

Tun da farko gwamnatin jihar ta sanar da kuɓutar da yara 15 a ranar 27 ga watan Afrilu.

A cikin sanarwar Fanwo bayyana nasarar baya-bayan nan da aka samu ta kuɓutar da yaran a matsayin wata gagaruma a yakin da jami’an tsaro ke yi da ɓata gari a jihar.

Kwamishinan ya kuma ya bawa dakarun Rundunar Sojan Najeriya Birged  ta 12 bayan da suka jagoranci sauran jami’an tsaro wajen kuɓutar da yaran a dajin Agbaja dake karamar hukumar Lokoja.

More from this stream

Recomended