Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta Da Ɗalibai 4 Yayin Jarabawar NECO A Kogi



Wasu ‘yan bindiga sun sace shugaban Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Olowa (GSS Olowa) da ke Ƙaramar Hukumar Dekina a Jihar Kogi, tare da ɗalibai 4 da kuma wani jami’in wucin gadi na NECO.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da yammacin Talata yayin da ake gudanar da jarabawar NECO, inda maharan suka kutsa cikin makarantar suka tafi da mutanen kafin jami’an tsaro su isa wurin.

Hukumomin tsaro sun ce sun fara aikin nema da ceto tare da ƙara sa ido da tattara bayanan sirri domin gano inda waɗanda aka sace suke da kuma kamo maharan.

Rahotanni sun kuma tabbatar da cewa ɗaya daga cikin ɗaliban da aka sace ya kuɓuta, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran mutanen da ke hannun masu garkuwa da mutanen.

More from this stream

Recomended