Gwamna Radda ya gana da sarakunan Katsina da Daura kan matsalar tsaro

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya gana da Sarkin Katsina, Mai Martaba Abdulmumin Kabir Usman da Sarkin Daura  Umar Faruku Umar da kuma hakimai da dagatai dake faɗin jihar Katsina domin tattauna matsalar tsaro da kuma wasu batutuwa da suka shafi al’ummominsu.

Taron ya hado kan sarakunan gargajiya da kuma manyan jami’an gwamnati inda suka sake duba ƙoƙarin da ake yi na magance matsalar tsaro, samar da  zaman lafiya da kuma samar da cigaban al’umma a fadin jihar baki ɗaya.

A yayin taron gwamna Radda ya jaddada muhimmancin haɗin kai mai ƙarfi a tsakanin gwamnati da kuma masu riƙe da masarautun gargajiya wajen magance matsalar tsaro ya ƙara da cewa sarakunan gargajiya na da muhimmanci wajen tattara bayanan sirri, sasanta rikici da kuma hadakan jama’a.

Ya yabawa rawar da sarakuna, hakimai da dagatai su ke takawa wajen goyon bayan matakan gwamnati na ɗorewar zaman lafiya a jihar.

More from this stream

Recomended