Dakarun Najeriya Sun Kuɓutar Da Mutum 9, Sun Ƙwato Dabbobi 56 A Katsina

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun kuɓutar da mutum 9 da aka yi garkuwa da su, sannan sun ƙwato dabbobi 56 da aka sace tare da kama wani da ake zargi da alaƙa da ayyukan ta’addanci a Jihar Katsina.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya ce an gudanar da waɗannan hare-hare ne bisa bayanan sirri a ƙananan hukumomin Faskari, Bakori da Danmusa.

Ya bayyana cewa mutanen da aka ceto sun tsere ne daga maboyar masu garkuwa bayan masu tsaron su sun yi barci, kafin dakaru su same su. Haka kuma, dakarun sun ƙwato shanu 4 da tumaki 52 da aka sace, yayin da ake ci gaba da binciken mutumin da aka kama.

More from this stream

Recomended