DA ƊUMI-ƊUMI: Kungiyoyin ƙwadago za su tsunduma yajin aiki ranar Litinin

Mambobin kungiyar kwadago, a ranar Juma’a, sun shelanta yajin aikin sai baba-ta-gani a fadin kasar saboda kin amincewar da gwamnatin tarayya ta yi na kara karin mafi karancin albashi daga N60,000.

Shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ke gudana a gidan ma’aikata dake Abuja.

Ajaero ya ce za a fara yajin aikin ne da tsakar daren ranar Lahadi 2 ga watan Yuni, 2024.

A ranar Juma’ar ne dai tattaunawa kan batun mafi karancin albashi tsakanin Gwamnatin Tarayya da kungiyoyin kwadago ta lalace a lokacin da gwamnatin ta kasa sauya sheka kan N60,000 da ta gabatar a taron da ya gabata.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]