
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana jagorancin jihar a matsayin babban ƙalubale saboda yawan al’ummarta da bambancin mutanen da ke zaune a cikinta.
Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ambasada Ibrahim Waiya, wanda ya wakilce shi a taron shekara-shekara na farko na Cibiyar Nazarin Tsaro da Harkokin Dabarun Tsaro (ISSS).
A cewar Gwamna Yusuf, yanayin Kano ya sa ta kasance tamkar “ƙaramar Najeriya”, saboda mutane daga sassa daban-daban na ƙasar suna zaune a jihar.
Ya ce: “Kamar yadda ɗaya daga cikin masu gabatar da jawabi a taron ya faɗa, jagoranci ba abu ne mai sauƙi ba. Ba aikin malalaci ba ne, domin kana jagorantar jiha wadda take tamkar ƙaramar Najeriya.
“Kano tana da yawan jama’a sosai, kuma kwanan nan an bayyana ta cikin biranen da suka fi yawan jama’a a duniya.
“Jiha ce mai cike da mutane daga sassa daban-daban, kuma matattarar ’yan Najeriya ce saboda mutane daga kusan dukkan sassan ƙasar suna zaune a Kano.
“Saboda haka, Kano ƙaramar Najeriya ce, kuma jagorancinta ba abu ne mai sauƙi ba.”
A wajen taron, an karrama Gwamna Yusuf da lambar yabo ta ƙwarewa a fannin tafiyar da harkokin tsaro. Waiya ya ce gwamnatin jihar ta haɗa matakan tsaro na ƙarfi da na lumana wajen magance rashin tsaro.
Ya ce kusan matasa 2,000 ne aka horas ƙarƙashin shirin Neighbourhood Watch, sannan aka tura su ƙananan hukumomi 44 domin tallafa wa jami’an tsaro.
Wani masani kan harkokin tsaro, Dakta Muhammad Ali, ya yi kira ga gwamnonin jihohin Arewa maso Yamma bakwai su ƙara haɗin kai da musayar bayanan sirri domin magance ’yan bindiga, satar shanu da sauran laifuka.
Ali ya ce haɗin kan gwamnonin zai taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro a yankin.