Atiku ya gana da Abdulaziz Yari a Abuja

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi wata ganawar sirri da tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari  a birnin tarayya Abuja.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa ganawar ta gudana ne a gidan Atiku dake Abuja kuma an yi ta ne a sirrance. Dukkanin  mutanen biyu Atiku da Yari babu wanda ya yiwa  yan jaridu jawabi akan ganawar ko kuma fitar da wata sanarwar kan dalilin  ganawar.

Ganawar ta su na zuwa ne a dai-dai lokacin da ake cigaba da raɗe-raɗi kan siyasar zaɓen 2027 ta yadda yan siyasa ke cigaba da tattaunawa da  kulla ƙawance don tunkarar zaben 2027.

Atiku  wanda  ya yiwa jam’iyyar PDP takarar zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2023 yanzu haka ya koma jam’iyyar ADC kuma tuni ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Ana sa bangaren Yari shi ne sanata dake wakiltar mazabar yammacin Zamfara a majalisar dattawa karkashin jam’iyar APC.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]