Zaɓen 2027: Malami Ya Zaɓi Musa Zagi A Matsayin Mataimakinsa a Takarar Gwamnan  Kebbi a ADC

Ɗan takarar gwamnan jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kebbi, Abubakar Malami, ya zaɓi Musa Zagi a matsayin mataimakin ɗan takararsa a zaɓen gwamna na 2027.

Jam’iyyar ta sanar da hakan ne cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaranta na jihar, Injiniya Abubakar Atiku Musa, ya fitar.

Sanarwar ta ce an amince da naɗin Musa Zagi, tare da bayyana kwarin gwiwar cewa zai iya sauke nauyin da ke kansa idan jam’iyyar ta yi nasara a zaɓen.

Jam’iyyar ta kuma taya sauran ‘yan takararta murna, tare da kira ga mambobi da magoya baya su kasance cikin haɗin kai. Haka kuma, ta buƙaci gudanar da zaɓe cikin lumana, adalci da gaskiya, tare da roƙon al’ummar jihar Kebbi su mara wa ‘yan takararta baya.

More from this stream

Recomended