Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) na ƙasa, Sanata David Mark, da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Rauf Aregbesola, sun kai ziyarar ta’aziyya ga tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi, bayan rasuwar mahaifiyarsa, Dame Ezinne Mary Oduah.
Jiga-jigan jam’iyyar sun jajanta wa Amaechi da iyalansa, tare da yi musu addu’ar samun haƙurin jure wannan rashi.
Haka kuma, tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma tsohon Ministan Shari’a, Dakta Abubakar Malami, SAN, ya kai irin wannan ziyara domin miƙa ta’aziyyarsa da addu’o’insa ga iyalan mamaciyar.
Sanata Aishatu Dahiru Binani, ‘yar takarar gwamnan ADC a jihar Adamawa, tare da mijinta, Farfesa Ahmed Modibbo, su ma sun ziyarci Amaechi domin jajanta masa kan rasuwar mahaifiyarsa.
David Mark, Aregbesola, Malami Da Wasu Sun Kai Wa Amaechi Ziyarar Ta’aziyya

