Aslam Aliyu ta hannun damar Atiku ta koma jam’iyar APC

Aslam Aliyu ta hannun daman tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ta sanar da ficewa daga jam’iyyar ADC inda ta koma jam’iyar APC.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi Aslam ta ce ta ɗauki matakin sauya shekar ne bayan dogon duba na tsakanaki kan alkiblar siyasar Najeriya da kuma damar yan adawa suke da ita na samar da wata gwamnatin da ta sha banban da irin ta yanzu.

” Kusan shekaru 20 ina aiki tukuru a tafiyar siyasar Atiku Abubakar ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyar ADC a zaɓen 2027 a cikin wannan shekaru ina biyayya ga tafiyar ɗari bisa ɗari,” a cewar sanarwar da ta fitar.

Ta ce yanzu a fili ta nuna ƙarara cewa yan adawa basu da wani shiri na samar da cigaba ko kuma wanda za a ceto al’ummar Najeriya.

Yar siyasar daga jihar Zamfara ta ce jam’iyar ADC bata da wani shiri a ƙasa da ya wuce sukar gwamnati ba tare da kawo hanyoyin magance matsalolin da suke addabar al’umma ba.

Da yake mata maraba da shiga jam’iyar APC, Nentawe Yilwatda shugaban jam’iyar APC na ƙasa ya ce shigar Aslam jam’iyar babban nasara ga jam’iyar.

More from this stream

Recomended