

Francis Fadahunsi sanata dake wakiltar mazabar gabashin jihar Osun a majalisar dattawa karkashin APC ya amsa gayyatar da rundunar yan sandan jihar Osun ta yi masa kan wani fefan bidiyonsa da ya karade soshiyal midiya inda a ciki yake kira da aka kashe yan jihar Accord Party.
Fadahunsi ya isa hedkwatar rundunar jihar dake Osogbo da misalin karfe 02:00 na ranar Laraba.
Rundunar yan sandan ta gayyaci sanatan ne domin ya yi karin haske kan kalaman da ya yi na tayar da hankali a lokacin da yake ganawa da magoya bayansa gabanin zaben gwamnan jihar da za a gudanar.
“Daga yanzu duk sanda kuka ga yan jam’iyar Accord Party ku kashe su. Umarni na ne ku kashe su har matansu da yara mata,” a cewar Fadahunsi lokacin da yake jawabi da harshen yarabanci.
Jawabin nasa ya jawo kakkausar suka daga mutane da dama a kafafen sadarwar zamani abun da ya kai ga gayyatarsa da rundunar yan sandan ta yi.
Da yake karin haske kan batun sanata Fadahunsi ya ce yana nufin aka kashe mutanen ne da ruwan kuri’u.