Gwamnatin jihar Osun ta kai karar hukumar EFCC gaban Kotu

Gwamnatin jihar Osun ta shigar da ƙarar hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja.

An shiga da ƙarar ne biyo bayan matakin da hukumar EFCC ta ɗauka na rufe asusun ajiyar banki na gwamnatin jihar.

A ƙarar da aka shigar ranar 5 ga watan Agusta mai lamba FHC/ABJ/CS/1762/2026 a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja masu ƙarar na neman kotun da ta soke umarnin na EFCC tare da umartar hukumar da ta biya gwamnatin Osun diyyar biliyan biyu.

Ademola Adeleke gwamnan jihar Osun, antoni janar na Osun da kuma babban akanta  janar su ne wadanda suka shigar da karar hukumar EFCC, shugabanta da kuma bankin First Bank.

A ranar Alhamis ne shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar EFCC da ta garzaya kotu domin neman umarnin janye umarnin da kotun ta bayar na rufe asusun ajiyar gwamnatin jihar Osun.

Tinubu ya ce matakin da hukumar EFCC ta ɗauka ya muzanta shi musamman idan aka yi duba da cewa kwanaki kaɗan su ka rage a gudanar da zaben kujerar gwamnan jihar.

More from this stream

Recomended