
Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ta kama wasu matasa uku da aka zargi da cin zarafin takardar kuɗin naira.
Jami’an hukumar da suka fito daga ofishin hukumar na shiyar Maiduguri ne suka kama matasan a birnin Maiduguri.
Matasan da aka kama sun haɗa da Adam Muhammad, Muhammad Muhammad da kuma Bashir Musa.
An kama Adam, Bashir da kuma Musa ne bayan a wani fefen bidiyonsu ya karade soshiyal midiya inda aka gansu suna share majina da takardar kuɗin naira ₦500.
Bayan sakin bidiyon ne jami’an hukumar suka gano mutanen uku suka kuma kama su a birnin Maiduguri.
Za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

