Ƴansanda sun kashe ɗan fashi tare da kama wasu uku

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe a ranar Juma’a ta ce ta kashe wani da ake zargin dan fashi da makami ne a wata fafatawa, yayin da aka kama wasu uku, sannan shida suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Sharif Saad, ya ce an sanar da sashen kula da rundunar ‘yan sandan cewa wasu gungun ‘yan fashi da makami da suka kware wajen addabar al’ummar garin Gombe, musamman a kwatas-kwatas ɗin Arawa, Malam Inna da Nayi Nawa.

Wani bangare na bayanin Saad ya kara da cewa, “’yan fashin sun kai farmaki gidan Alhaji Gidado Muhammad Sani da ke unguwar Arawa, inda suka yi ta harbe-harbe tare da yi musu fashin dukiyoyinsu.”

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...