Ƴansanda sun kashe ɗan fashi tare da kama wasu uku

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe a ranar Juma’a ta ce ta kashe wani da ake zargin dan fashi da makami ne a wata fafatawa, yayin da aka kama wasu uku, sannan shida suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Sharif Saad, ya ce an sanar da sashen kula da rundunar ‘yan sandan cewa wasu gungun ‘yan fashi da makami da suka kware wajen addabar al’ummar garin Gombe, musamman a kwatas-kwatas ɗin Arawa, Malam Inna da Nayi Nawa.

Wani bangare na bayanin Saad ya kara da cewa, “’yan fashin sun kai farmaki gidan Alhaji Gidado Muhammad Sani da ke unguwar Arawa, inda suka yi ta harbe-harbe tare da yi musu fashin dukiyoyinsu.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]