Ƴansanda sun kashe ɗan fashi tare da kama wasu uku

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe a ranar Juma’a ta ce ta kashe wani da ake zargin dan fashi da makami ne a wata fafatawa, yayin da aka kama wasu uku, sannan shida suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Sharif Saad, ya ce an sanar da sashen kula da rundunar ‘yan sandan cewa wasu gungun ‘yan fashi da makami da suka kware wajen addabar al’ummar garin Gombe, musamman a kwatas-kwatas ɗin Arawa, Malam Inna da Nayi Nawa.

Wani bangare na bayanin Saad ya kara da cewa, “’yan fashin sun kai farmaki gidan Alhaji Gidado Muhammad Sani da ke unguwar Arawa, inda suka yi ta harbe-harbe tare da yi musu fashin dukiyoyinsu.”

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]