
Jam’iyar ADC ta ce hukuncin da kotun daukaka kara dake Abuja ta yanke a ranar Litinin na da alaƙa ne kaɗai da zaɓukan shugabannin jam’iyar a mazaɓu, ƙananan hukumomi da kuma jiha ba wai zaɓen fitar da gwani ba.
Mai magana da yawun jam’iyar, Mallam Bolaji Abdullahi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.
Abdullahi na mayar da martani ne kan hukuncin kotun dauka kara inda ya tabbatarwa da yan jam’iyar dama sauran al’umma baki ɗaya cewa hukuncin bashi da alaƙa ta kusa ko ta nesa kan zaɓen fidda gwani na yar tinke da jam’iyar ta gudanar inda aka zaɓi yan takarkaru a matakai daban-daban.
ADC ta ta bayyana cewa tuni jam’iyar ta fara shirin daukaka kara kan hukuncin kotun.
.

