Ƴan bindiga sun kashe jami’in NDLEA tare da yin garkuwa da mutane 3 a Sokoto

Wasu ƴan bindiga da ba’asan ko suwaye ba sun harbe wani jami’in hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun ƙwayoyi kana suka kuma yi garkuwa da wasu mutane 3 akan titin zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar dake Sokoto.

Wani mazaunin yankin da abun ya faru, Muhammad Baba Usman wanda ɗansa na daga cikin waɗanda aka sace ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne da misalin ƙarfe 09:30 na dare.

“Su huɗu ne dukkaninsu ɗauke da bindiga. Sun zo a cikin mota da suka ajiye ta a bakin titi.Dukkansu sun fito suka fara harbin kan me uwa da wabi mutum guda harsashi ya sama ya kuma mutu akan hanyar zuwa asibiti,”

“Sun kuma yi awon gaba da mutane uku ciki har ɗa na. Har yanzu muna jiran kiran wayarsu muji abun da za su buƙata.” A cewar Muhammad

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmed Rufa’i ya tabbatar da cewa wanda ya mutu ma’aikci ne a hukumar NDLEA.

A cewar Rufa’i ƴan sanda na bin sawun masu garkuwa da mutanen.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...