Wasu ƴan bindiga da ba’asan ko suwaye ba sun harbe wani jami’in hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun ƙwayoyi kana suka kuma yi garkuwa da wasu mutane 3 akan titin zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar dake Sokoto.
Wani mazaunin yankin da abun ya faru, Muhammad Baba Usman wanda ɗansa na daga cikin waɗanda aka sace ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne da misalin ƙarfe 09:30 na dare.
“Su huɗu ne dukkaninsu ɗauke da bindiga. Sun zo a cikin mota da suka ajiye ta a bakin titi.Dukkansu sun fito suka fara harbin kan me uwa da wabi mutum guda harsashi ya sama ya kuma mutu akan hanyar zuwa asibiti,”
“Sun kuma yi awon gaba da mutane uku ciki har ɗa na. Har yanzu muna jiran kiran wayarsu muji abun da za su buƙata.” A cewar Muhammad
Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmed Rufa’i ya tabbatar da cewa wanda ya mutu ma’aikci ne a hukumar NDLEA.
A cewar Rufa’i ƴan sanda na bin sawun masu garkuwa da mutanen.