Mutum 4 Sun Mutu, An Kuɓutar Da Mutum 32 Bayan Harin ’Yan Bindiga A Sokoto



Rundunar ƴansandan Jihar Sokoto ta sanar da cewa mutum 4 sun rasa rayukansu bayan harin da wasu ’yan bindiga suka kai ƙauyen Maikujera da ke ƙaramar hukumar Rabah.

A cewar rundunar, maharan sun yi garkuwa da mutane tare da satar dabbobi kafin jami’an tsaro da sojoji su kai ɗauki bayan samun kiran gaggawa.

Rundunar ta ce an yi musayar wuta tsakanin jami’an tsaro da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa zuwa cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su da kuma dabbobin da suka sace.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kuɓutar da mutum 32 ba tare da sun ji rauni ba. Waɗanda aka ceto sun haɗa da maza 6 da mata 26, yawancinsu yara ne.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar maharan domin gurfanar da su a gaban shari’a.

More from this stream

Recomended