Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutane 10 da aka yi garkuwa da su bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a ƙauyen Badanma da ke ƙaramar hukumar Gandi a jihar Sokoto.
Rahotanni sun ce sojojin sun gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar Rundunar Tsaron Al’umma ta Jihar Sokoto bayan samun sahihan bayanan sirri kan motsin maharan.
An ce ƙarfin wutar da jami’an tsaron suka yi amfani da shi ya tilasta wa ‘yan bindigar tserewa, inda suka bar mutanen da suka sace. Dukkan mutanen da aka ceto sun tsira ba tare da sun ji rauni ba.
Jami’an tsaro sun ce suna ci gaba da farautar maharan tare da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da satar mutane da ayyukan ‘yan bindiga a jihar Sokoto.
Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Sokoto

