‘Yan Sanda Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Sakkwato



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Sakkwato ta ce ta daƙile wani hari da ake zargin ‘yan bindiga sun kai ƙauyen Daraye da ke Ƙaramar Hukumar Wamakko.

A cewar rundunar, jami’anta sun yi musayar wuta da maharan, lamarin da ya sa suka tsere zuwa cikin daji. Daga baya, jami’an sun kashe mutum ɗaya da ake zargin ɗan bindiga ne tare da ƙwato bindigar AK-47 guda ɗaya da harsasai 28.

Rundunar ta bayyana cewa ta ƙara yawan sintirin tsaro a yankin, kuma tana ci gaba da neman sauran waɗanda suka tsere domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

More from this stream

Recomended