Zanga-zanga:Matasa garin Suleja sun rufe hanyar Abuja zuwa Kaduna 

Wasu matasa sun fantsama kan tituna inda suke zanga-zanga kan tsananin matsin rayuwa da ake fama da shi a ƙasarnan.

Zanga-zangar ta su na zuwa ne kwanaki biyu gabanin fara zanga-zangar da aka shirya farawa a ranar 1 ga watan Agusta.

Amma kuma wasu matasa a garin Suleja dake jihar Niger sun yi riga malam masallaci inda suka fantsama kan tituna ɗauke da kwalaye da aka rubuta “Dole a dawo da tallafin mai” ” Ya isa haka ya isa haka” ” Mu ba bayi bane ƙasarmu” da sauran rubututtuka makamantan haka.

Masu zanga-zangar na jerin gwano ne akan babbar hanyar Abuja-Kaduna ta ratsa garin na Suleja inda suke faɗin kalaman nuna ƙin jinin gwamnati.

Gwamnonin jihohi da kuma shugaban ƙasa sun yi kiraye-kiraye ga matasa da su janye batun zanga-zangar da suke shirin gudanarwa.

Suma jami’an tsaro sun gargadi masu shirya-shirya zanga-zangar cewa wasu ɓata gari ka iya amfani da damar wajen tayar da zaune tsaye.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]