Matasa a Abuja sun yi zanga-zanga kan matsalar tsaro

Wasu mutane da suka gudanar da zanga-zanga a birnin tarayya Abuja sun bukaci gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya ceto yara ɗalibai yan makaranta da kuma malaman su dake hannun masu garkuwa da mutane.

Masu zanga-zangar sun mamaye gadar Nyanya-Karu dake Abuja domin gabatar da bukatunsu.

Zanga-zangar ta haifar da cunkoson ababen hawa a hanyar har sai da ta kai ga sojoji sun kawo ɗauki inda suka kawar da mutanen.

Masu zangar sun rika kiran ” Dole Tinubu ya sauka, ka dawo mana da yaranmu,” a yayin da suke ɗauke da kwalaye da aka rubuta  a kuɓutar da yara da kuma malaman da aka ɗauke a jihohin Oyo da Borno.

Martins Vincent Otse da aka fi sani da Very Darkman wanda ke fafutuka a kafafen sadarwar na ɗaya daga cikin waɗanda suka shiga zanga-zangar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]