Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Harin Bam Na Nyanya


Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa Zakaria Garba mai shekara talatin da bakwai hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda hannu da ake zargin yana da shi a harin bam na Nyanya da aka kai a shekarar 2014.

Mai shari’a James Omotosho ne ya yanke hukuncin yayin shari’ar wadanda ake zargi da laifukan ta’addanci a babban birnin tarayya.

Garba ya amsa laifuffuka biyar da ake tuhumarsa da su bayan Ofishin Antoni Janar na Tarayya ya shigar da karar.

Harin bam din Nyanya ya faru ne a watan Afrilun shekarar dubu biyu da goma sha hudu, inda sama da mutum saba’in suka mutu sannan wasu da dama suka jikkata.

Kotun ta yanke masa hukuncin daurin shekaru talatin da biyar kan tuhume-tuhume biyu na farko, daurin rai da rai kan tuhuma ta uku, sannan hukuncin kisa ta hanyar rataya kan tuhume-tuhume na hudu da na biyar.

Mai shari’ar ya ce amsa laifin da wanda ake tuhuma ya yi tare da hujjojin da aka gabatar sun tabbatar da hannunsa a harin.

More from this stream

Recomended