’Yan Bindiga Sun Kashe Tsohon Soja Tare Da Sace Mata a Nasarawa



Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon soja tare da yin garkuwa da wata mata a wani hari da suka kai a yankin da ke iyakar Jihar Nasarawa da Abuja.

Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne da daddare a kusa da Jikwoyi, inda suka shiga gidan wani mutum mai suna Silas Orite suka sace matarsa, Bukola Oluwatoyin Silas.

Wani tsohon soja mai ritaya, Reuben Yelwa mai shekara 61, ya yi ƙoƙarin taimaka wa iyalan da aka kai wa harin, amma maharan suka harbe shi har lahira.

Bayan faruwar lamarin, jami’an tsaro sun isa yankin tare da fara bincike, yayin da hukumomi suka ce ana ci gaba da ƙoƙarin ceto matar da aka sace da kuma kamo waɗanda suka kai harin.

Hukumomin tsaro sun kuma ce an ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin domin hana sake aukuwar irin wannan hari.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]