Zaɓaɓɓen Gwamnan Sokoto Ya Ƙaryata Batun Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Gwamnatin Tambuwal

Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu ya musalta kafa kwamitin da zai binciki gwamna mai barin gado, Aminu Waziri Tambuwal.

Bayanin haka na kunshe ne cikin wata sanarwa da Abubakar Bawa mai magana da yawun zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar a ranar Alhamis.

A cikin sanarwar zaɓaɓɓen gwamnan ya bayyana cewa baki ɗayan labarin kirkirarre ne babu kanshin gaskiya a ciki

Sanarwar ta kara da cewa a iya sanin gwamnan an kafa kwamiti ne na karɓar mulki da zai aiki tare da kwamitin mika mulki da gwamnatin jihar ta kafa.

Zaɓaɓɓen gwamnan ya ƙara da cewa har yanzu bai karbi ragamar jagorancin mulkin jihar ba ballantana ya kafa kwamitin bincike.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...