Rundunar yan sandan jihar Kaduna ta kama mutane 10 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a tsakanin watan Satumba zuwa ranar 3 ga watan Oktoba.
Mai rikon muƙamin kakakin rundunar, ASP Mansur Hassan shi ne ya bayyana haka a wurin wani taron manema labarai ranar Asabar a Kaduna.
Ya ce rundunar ta samu nasarar kwato bindigar AK-47 guda uku, karamar bindiga kirar gida guda uku mai cin harsashi 10, harsashi 448 da sauransu.
Har ila yau rundunar ta gano wata mai É—auke da namba Ebonyi HKW 578 AA.
Mai magana da yawun rundunar ya ce kwamishinan yan sandan jihar Musa Garba ya yabawa jami’an kan gwarzantaka da suka nuna da kuma sadaukarwa ga aiki.