Wani mekaniƙi mazaunin Kaduna, Aliyu Muhammed, ya zargi wasu jami’an ’yan sanda da mika matarsa, Ummulkhairi Muhammed, ga wasu fusatattun mutane da suka kashe ta tare da kona gawarta bayan zargin safarar yara.
Aliyu mai shekaru 42 ya ce lamarin ya faru ne a yankin Mararaban Jos da ke karamar hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
Ya bayyana cewa matarsa ta fita zuwa makarantar Islamiya a wata unguwa makwabta ranar da aka kai harin, yayin da shi kuma ya tafi Kaduna domin aiki.
A cewarsa, daga baya wani mutum ya amsa kiran wayar matarsa sannan ya sanar da shi cewa wasu mata sun zarge ta da yunkurin safarar yara.
Aliyu ya ce ya tuntubi wani abokinsa domin ya kai dauki, inda daga baya aka sanar da shi cewa an kai matarsa ofishin ’yan sanda bayan an ceto ta daga hannun jama’a.
Sai dai ya yi zargin cewa jami’in ’yan sanda na yankin ya fito da matarsa daga cikin ofishin duk da rokon da iyalanta suka yi.
Ya ce, “The DPO held my wife’s hand and started dragging her towards the station gate.”
Aliyu ya kara da cewa bayan an fitar da ita, taron jama’a ya dinga dukanta kafin daga bisani su kona ta tare da baburinta.
Mijin marigayiyar ya bukaci a gudanar da cikakken bincike kan rawar da jami’an ’yan sanda suka taka a lamarin, musamman jami’in yankin da ake zargi da fitar da ita zuwa hannun jama’a.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su guji daukar doka a hannunsu, su bar jami’an tsaro da kotuna su gudanar da aikinsu.
Mijin Ummulkhairi Ya Zargi ’Yan Sanda Da Mika Matarsa Ga Taron Fusatattun Mutane Masu Ɗaukan Doka a Hannu

