Yan bindiga sun kai hari kan ofishin yan sanda a Kogi

Da tsakar daren ranar Juma’a Æ´an bindiga suka kai hari kan ofishin shiya na yan sanda dake Eika Ohizenyi a karamar hukumar Okehi ta jihar Kogi inda suka kashe wani Insifecta Jibril dake bakin aiki.

Wani mazaunin yankin, Mallam Momoh Abubakar ya bayyana cewa maharan sun mamaye ofishin yan sandan da misalin 12:15 na tsakar daren ranar Juma’a dauke da bama-bamai da sauran makamai.

Ya bayyana cewa bom na farko da suka jefa kan ofishin ya yi karar gaske da ta tashi mutane da dama daga bacci a yankin ya kara da cewa bama-baman sun lalata wani sashe na ginin ofishin.

Abubakar ya kara da cewa maharan sun ci karensu babu babbaka inda suka shafe sama da sa’o’i biyu ba tare da wani É—auki ba daga jami’an tsaro ko kuma mutanen gari.

Ya bayyana cewa jami’in dan sanda É—aya tilo dake bakin aiki, Jibril wanda aka fi sani da Yellow an kashe shi a harin yayin da aka lalata motar sintiri É—aya da ofishin yake da ita.

Yan bindigar sun lalata tagogin babban masallacin Eika da kuma na cocin Katolika dake garin.

Tuni kwamishinan yan sandan jihar, Edward Egbuka ya bada umarnin tura karin jami’an tsaro zuwa yankin.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...