

Mutane biyu aka kashe a yayin da wani mutum guda ya samu rauni a wasu hare-hare da aka kan wasu al’ummomi dake ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato.
Mai magana da yawun kungiyar Berom Youth Moulders Association, Rwang Tengwog ya tabbatarwa da yan jarida faruwar lamarin ranar Laraba a Jos babban birnin jihar.
A cewar kungiyar farmakin da aka kai da daren ranar Talata an kai shi ne ƙauyukan huɗu da suka haɗa da Gwa-Wereng, Rim, kauyen Kyeng dake gundumar Bachi da kuma ƙauyukan Dorong da Jol .
Lyop Gabriel wani mazaunin ɗaya daga cikin yankin da aka kai harin ya ce an kai farmaki kauyen Gwa-Wereng da misalin karfe 09:30 na dare lokacin da yan bindiga suka mamaye kauyen tare da budewa mutane wuta.
Tengwong ya ce yan bindiga sun kashe wani mutum mai suna Stephen Dachollom dake kauyen Kyeng a yayin suka kashe Bulus Mwagwong wanda aka fi sani da Dikko suka kuma jiwa ɗan uwansa mai suna Yakubu mummunan rauni.