
Wata kotu a jihar Neja ta yanke wa wani matashi mai suna Aliyu Bala hukuncin ɗaurin shekara 13 a gidan yari bayan ta same shi da laifin yi wa wata yarinya mai shekaru 10 fyaɗe.
Kotun ta kuma umarci a yi wa Bala bulala 20 a bainar jama’a tare da biyan yarinyar diyyar N250,000.
Bayan yanke hukuncin, an kai Bala fadar Hakimin Bosso, inda aka aiwatar da hukuncin bulalar a gaban jama’a.
Daraktar-Janar ta Hukumar Kare Haƙƙin Yara ta Jihar Neja, Barrister Ummul-Kalthume Muhammad, ta ce hukuncin ya nuna cewa gwamnatin jihar ba za ta yi wasa da laifukan cin zarafin yara ba.
Ta ce hukuncin ya zama gargaɗi ga duk wanda ke tunanin zai iya aikata laifin cin zarafin yara ba tare da fuskantar hukunci ba.
Hukumar ta jaddada cewa duk wanda ya aikata irin wannan laifi zai fuskanci hukunci mai tsauri kamar yadda doka ta tanada.