Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida.

Ƴan matan – Duro-Aina Adebola, Akindele Abiola, Faleke Oluwatoyin, da Bello Eniola sun baje kolin kere-keren nasu ne a taron shekara-shekara na Maker Faire Africa, da aka gudanar a Legas. 

Abiola, Oluwatoyin da Eniola sun fito da wata hanya mai amfani don aiwatar da wannan tunanin kuma gidaje da yawa za su iya amfani da shi.

RusselSmith, babbar jami’ar samar da Integrated Energy Solutions ta bayyana hakan, inda ta kara da cewa Adebola, ‘yar shekara 14, ta ce manufar yin amfani da fitsari wajen samar da wutar lantarki ta faro ne a lokacin da ta karanta labarin wasu mutane biyar da suka rasa rayukansu.

Ta ce sun mutu ne sakamakon gubar carbon monoxide yayin da suke shakar hayakin da ke fitowa daga janaretonsu a lokacin da suke barci.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...