Tsoron ƴan bindiga ya sa manoma kwashe amfanin gonar da bai karasa nuna ba a jihar Katsina

Manoma a wasu sassan jihar Katsina sun shiga tsaka mai wuya sakamakon yadda ƴan bindiga suke saka shanu suna lalata musu kayan amfanin gona.

Manoman sun bayyana da zarar kayi korafi ƴan bindiga ka iya harbe mutum nan take.

Rahotanni sun nuna cewa manoman suna kwashe amfanin gonar su duk da cewa bai gama karasawa domin gujewa asara.

Garuruwan da suke ƙaramar hukumar Sabuwa na daga cikin wuraren da lamarin yafi kamari.

Wasu mazauna garin Dugun Mu’azu sun koka kan yadda hukumomi su gaza kawo musu ɗauki kan halin da suka samu kansu a ciki.

More News

Wani mutumi ya yi garkuwa tare da kashe ƴar’uwarsa a Kaduna

A ranar Lahadin ne mazauna birnin Zariya na jihar Kaduna suka shiga alhini cikin alhini sakamakon kama wani mai suna AbdulAzeez Idris da ake...

Ɗan ta’addar Boko Haram ya miƙa kansa ga sojoji

Alhaji Wosai wani mamba a ƙungiyar ƴan ta'addar Boko Haram ya miƙa kansa ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai. Rahotanni sun bayyana...

An kuɓutar da wasu ɗaliban da aka sace a jami’a a Kogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta bayyana cewa an ceto 14 daga cikin daliban jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara Okene...

Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar...