Tinubu ya miƙa tuta ga ƴan takarar APC a zaɓukan gwamna na jihohin Kogi, Bayelsa da Imo

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya miƙa tuta ga yan takarar gwamna a jam’iyar APC a zaɓen da za ayi a jihohin Bayelsa, Kogi da kuma Imo.

A ranar 11 ga watan Nuwamba ne aka shirya gudanar da zaɓukan gwamna a jihohin uku.

Ƴan takarar na jam’iyar APC sun haɗa da Hope Uzodimma wanda yake neman a sake zaɓensa a matsayin gwamnan jihar Imo, sai Timpre Sylva a jihar Bayelsa da kuma Usman Ododo wanda yake neman a zaɓe shi a matsayin gwamnan Kogi.

Tinubu ya yi kira da a gudanar da sahihin zaɓe ba tare da tahin hankali ba.

A yan kwanakin nan hukumar zaɓe mai zaman kanta ƙasa INEC ta nuna damuwarta kan yadda ake yawan samun rikice-rikice da ya shafi ƴan takara da kuma jam’iyunsu a jihohin uku

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...