Sojoji sun kashe wani fitaccen ɗan bindiga a Kebbi

Sojoji sun samu nasarar kashe wani fitaccen ɗan bindiga da ake kira da Mainasara a wani gumurzu da aka yi a dajin Sangeko dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi.

Abdulrahman Usman daraktan tsaro a fadar gwamnatin jihar shi ne ya tabbatar da rahoton inda ya ce an kuma kashe karin wasu yan bindiga biyu dake da alaka da Mainasara.

Ya ce da misalin karfe 07:30 na safe ne sojojin dake sintiri a dajin Sengeko suka yi arangama da yan bindigar.

A yayin musayar wutar ne aka kashe ƴan bindiga a lokacin da suke ƙoƙarin tserewa a yayin da aka samu babura biyu na yan bindigar.

Usman ya shawarci mazauna jihar da su bawa jami’an tsaro duk ganin gudummawar da suke bukata domin raba jihar da ɓata gari.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...