Sojoji sun samu nasarar kashe wani fitaccen ɗan bindiga da ake kira da Mainasara a wani gumurzu da aka yi a dajin Sangeko dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi.
Abdulrahman Usman daraktan tsaro a fadar gwamnatin jihar shi ne ya tabbatar da rahoton inda ya ce an kuma kashe karin wasu yan bindiga biyu dake da alaka da Mainasara.
Ya ce da misalin karfe 07:30 na safe ne sojojin dake sintiri a dajin Sengeko suka yi arangama da yan bindigar.
A yayin musayar wutar ne aka kashe ƴan bindiga a lokacin da suke ƙoƙarin tserewa a yayin da aka samu babura biyu na yan bindigar.
Usman ya shawarci mazauna jihar da su bawa jami’an tsaro duk ganin gudummawar da suke bukata domin raba jihar da ɓata gari.