Rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta ayyana neman wani jami’inta mai suna Mohammed Yusuf Amutu ruwa a jallo bisa zargin sayar da kakin soji ga ƴan ta’adda da masu aikata laifuka.
Rahotanni sun ce jami’in ya tsere daga wurin aikinsa, kuma rundunar ta ce tana ƙoƙarin gano inda yake domin kama shi.
Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta lamunci duk wani jami’i da ke taimaka wa ƴan ta’adda ko sauran masu aikata laifuka ta hanyar sayar musu da kayan aikin soji ba, tare da bayyana cewa duk wanda aka kama da irin wannan laifi zai fuskanci hukunci bisa dokokin soji da kundin tsarin mulkin ƙasa.
Sojojin Najeriya Na Neman Jami’insu Ruwa A Jallo Kan Zargin Sayar Da Kakin Soji Ga Ƴan Ta’adda

