PDP Ta Soki Yadda Aka “Abkawa” Masu Zanga-zanga

Masu zanga-zanga a wasu biranen kasar sun yi gangami a ranar Asabar don bayyana korafe-korafensu kan yadda gwamnatin APC mai mulki ke tafiyar da al’amuran kasar.

“Jam’iyyar PDP na Allah wadai da kakkausar murya, kan yadda sojojin haya na APC da Shugaba Muhammadu Buhari suka abkawa ‘yan Najeriya masu zanga-zangar lumana a ranar dimokradiyya.” Wata sanarwa dauke da sa hannun Sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Kola Ologbondiyan ta ce.

Najeriya ta yi bikin ranar Dimokradiyya 12 ga watan Yuni.

“Abin ya yi banbarakwai, a ce jam’iyyar APC da Shugaba Buhari, sun zabi su gallazawa ‘yan Najeriya ta hanyar amfani da makamai kamar yadda aka gani, duk da cewa, a lokacin da suka yi zanga-zangarsu a shekarar 2014 an bar su sun yi cikin kwanciyar hankali.”

Yadda 'yan sanda suka yi amfani da hayaki mai sa kwalla wajen tarwatsa masu zanga-zanga a Legas
Yadda ‘yan sanda suka yi amfani da hayaki mai sa kwalla wajen tarwatsa masu zanga-zanga a Legas

Rahotanni da dama sun ruwaito cewa ‘yan sanda sun yi amfani da hayaki mai sa kwalla wajen tarwatsa masu zanga-zangar a biranen Abuja da Legas.

A cewar PDP, “ba abin mamaki ba ne, da shugaban ya kwashe sama da minti 20 yana jawabi (a jajiberin dimokradiyya) amma ya ki ya ambaci batun ‘yancin fadin albarkacin baki da yin taruka da kuma yin zanga-zangar lumana kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya tanada.”

Kokarin jin martanin jam’iyyar ta APC da hukumomin tsaro kan zargin na PDP bai yi nasara ba.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...